world-service-rss

BBC News Hausa

Shin ƴan hamayya za su iya dunƙulewa kafin 2027?

Shin ƴan hamayya za su iya dunƙulewa kafin 2027?

Asabar 26 Yuli, 2025 da 4:04:26 Safiya

Abubuwan da suka faru a baya-bayan nan tsakanin jam’iyyun hamayya inda suke nuna walle-walle da juna na jefa shakku a zukatan masu nazarin kimiyyar siyasa dangane da yiwuwar dunƙulewarsu wuri guda wajen ƙalubalantar jam’iyya mai mulki a 2027.

Ma’aikatar ilimin Najeriya ta musanta ƙayyade shekara 12 kafin shiga JSS1

Ma'aikatar ilimin Najeriya ta musanta ƙayyade shekara 12 kafin shiga JSS1

__

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Juma’a 26 ga watan Yulin 2025.

Newcastle na son Larsen, Wilson ya daidaita da West Ham

Newcastle na son Larsen, Wilson ya daidaita da West Ham

Asabar 26 Yuli, 2025 da 4:06:21 Safiya

Newcastle United ta kwaɗaitu da ɗan wasan Wolves’ mai shekara 25 daga Norway, Jorgen Strand Larsen.

‘Ƙawayen Isra’ila sun fara ƙaurace mata’: Ƙasashen duniya sun fara juya wa Netanyahu baya

'Ƙawayen Isra'ila sun fara ƙaurace mata': Ƙasashen duniya sun fara juya wa Netanyahu baya

Asabar 26 Yuli, 2025 da 4:03:15 Safiya

Rahotanni na nuna cewa hatta shugaban Amurka, babbar ƙawar Isra’ila, Donald Trump ya ƙule da Netanyahu bayan da Firaiministan na Isra’ila ya mamayi Amurka wajen kai hari a Syria, kan sabuwar gwamnatin da Trump ya amince da ita.

Yadda zaftare tallafin Birtaniya zai yi illa ga Afirka

Yadda zaftare tallafin Birtaniya zai yi illa ga Afirka

Asabar 26 Yuli, 2025 da 4:03:56 Safiya

Gwamnatin Birtaniya ta bayyana shirinta na rage tallafin ƙasashen waje, kuma tallafin karatun yara da na ilimin mata a Afirka ne ke fuskantar zaftarewa mafi girma.

Yaƙin Cambodia da Thailand ya tsananta

Yaƙin Cambodia da Thailand ya tsananta

Asabar 26 Yuli, 2025 da 6:43:20 Safiya

Yaƙin ya janyo asarar sama da mutum talatin da kuma dubbai da suka bar muhallinsu, tun bayan da rikicin kan iyakar ya ɓarke kwatsam ranar Alhamis.

Kwankwaso ya yi kuskure, Tinubu bai manta da Arewa ba — Fadar Shugaban ƙasa

Kwankwaso ya yi kuskure, Tinubu bai manta da Arewa ba — Fadar Shugaban ƙasa

__

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Juma’a 25 ga watan Yulin 2025.

Kirista mai nakasa da ke gina rayuwar matasan Musulmi a arewacin Najeriya

Kirista mai nakasa da ke gina rayuwar matasan Musulmi a arewacin Najeriya

Jummaʼa 25 Yuli, 2025 da 6:09:48 Yamma

Chris ya ce bambancin addini ne ke jawo rikice-rikice, wanda a cewarsa ke jawo tashe-tashen hankula da kashe-kashe.

Abubuwan da suka kamata ku sani kan marigayi Hulk Hogan

Abubuwan da suka kamata ku sani kan marigayi Hulk Hogan

Jummaʼa 25 Yuli, 2025 da 12:13:35 Yamma

Hulk Hogan, ɗaya daga cikin mafiya shahara a wasan kokawa na reslin, ya mutu yana da shekara 71.

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

__

Wannan shafi ne da ke kawo muku sharhi da bayanan wasanni a faɗin duniya daga Asabar 19 - 25 ga watan Yulin 2025.

Liverpool na farautar Isak, Wataƙil Sterling ya je Napoli

Liverpool na farautar Isak, Wataƙil Sterling ya je Napoli

Jummaʼa 25 Yuli, 2025 da 4:01:17 Safiya

Liverpool na shirin gabatar da tayi kan ɗan wasan Newcastle da Sweden, Alexander Isak mai shekara 25.

Ƴanwasan Najeriya mata biyar da tarihi ba zai manta da su ba

Ƴanwasan Najeriya mata biyar da tarihi ba zai manta da su ba

Alhamis 24 Yuli, 2025 da 12:45:10 Yamma

Abu na farko da mutum zai fara ji game da tawagar ƙwallon ƙafa ta matan Najeriya shi ne ta lashe kofin ƙasashen Afirka sau tara, mafi yawa kenan a tarihin gasar.

Napoli na son Grealish, Tottenham na sa ido kan Mainoo

Napoli na son Grealish, Tottenham na sa ido kan Mainoo

Alhamis 24 Yuli, 2025 da 4:10:54 Safiya

Ɗanwasan Manchester City da Ingila Jack Grealish mai shekara 29, na cikin waɗanda Napoli ke zawarci.

Najeriya ta lallasa Afirka ta Kudu ta kai wasan ƙarshe a gasar cin kofin Afirka ta mata

Najeriya ta lallasa Afirka ta Kudu ta kai wasan ƙarshe a gasar cin kofin Afirka ta mata

Talata 22 Yuli, 2025 da 10:02:49 Yamma

Najeriya ta samu nasarar zura ƙwallo ta biyu gab da za a tashi wasa, lamarin da ya kawo ƙarshen mafarkin Afirka ta Kudu na kare kambinta, inda aka tashi Najeriya na da ci biyu Afirka ta Kudu kuma na da ɗaya.

Me ya sa kallo ya koma kan Kwankwaso?

Me ya sa kallo ya koma kan Kwankwaso?

Jummaʼa 25 Yuli, 2025 da 4:00:11 Safiya

A makon nan sunan tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso shi ne yake ta faman amo a muhawara da tattaunawa a shafukan sada zumunta da ma a zahiri.

An yi jana’izar marigayi Sarkin Gusau Ibrahim Bello

An yi jana'izar marigayi Sarkin Gusau Ibrahim Bello

Jummaʼa 25 Yuli, 2025 da 4:11:57 Yamma

Sanarwar da gwamnatin jihar Zamfara ta fitar ta ce: “rasuwar mai martaba babban rashi ne ga jihar Zamfara da ma daukacin arewacin Najeriya”.

Ba zan bi Obi haɗakar ADC ba - Datti Baba-Ahmed

Ba zan bi Obi haɗakar ADC ba - Datti Baba-Ahmed

Jummaʼa 25 Yuli, 2025 da 4:03:11 Safiya

'’Wace ce ADC? Me ya sa zan saki reshe in kama ganye? Su wane ne shugabannin haɗakar? Ba na cikin waɗanda ke biye wa mutane, a rufe ido a rufe tunani a yi ta hauka.’’

Faransa za ta amince da kafuwar ƙasar Falasɗinu - Macron

Faransa za ta amince da kafuwar ƙasar Falasɗinu - Macron

Jummaʼa 25 Yuli, 2025 da 4:06:40 Safiya

Amurka da Isra’ila sun yi kakkausar suka ga matakin na Faransa, yayin da Saudiyya ta yaba da cewa tarihi ne, kamar yadda hukumomin Falasɗinawa suka yi maraba da shi.

Me ya sa Thailand da Cambodia ke faɗa?

Me ya sa Thailand da Cambodia ke faɗa?

Jummaʼa 25 Yuli, 2025 da 4:00:43 Safiya

Artabu tsakanin sojojin Thailand da Cambodia a kan iyakar ƙasashen da ake rikici a kai, ya janyo mutuwar mutum 12, a cewar hukumomin Thailand.

‘Motocin agaji 6,000 ne ke jira don samun izinin shiga Gaza’

'Motocin agaji 6,000 ne ke jira don samun izinin shiga Gaza'

__

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 24 ga watan Yulin 2025.

APC ta nada Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugabanta

APC ta nada Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugabanta

Alhamis 24 Yuli, 2025 da 9:57:31 Safiya

Kwamitin zartarwa na Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, ya amince da nadin Farfesa Nentawe Yilwalda daga jihar Filato a matsayin sabon shugaban jam’iyyar na kasa.

Gwamnatin Tinubu ta yi watsi da yankin arewa - Kwankwaso

Gwamnatin Tinubu ta yi watsi da yankin arewa - Kwankwaso

Alhamis 24 Yuli, 2025 da 6:32:23 Yamma

Tsohon gwamnan jihar Kano, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya caccaki gwamnatin Bola Tinubu kan abin da ya kira watsi da yankin arewacin Najeriya, inda ya ce shugaban ya fi mayar da hankali kan gina kudancin ƙasar ta hanyar amfani da albarkatun ƙasar.

Yin tattaki kafa 7,000 a kullum na rage haɗarin kamuwa da cututtuka - Bincike

Yin tattaki kafa 7,000 a kullum na rage haɗarin kamuwa da cututtuka - Bincike

Alhamis 24 Yuli, 2025 da 5:55:38 Yamma

Yin tattaki kafa 7,000 a kullum shi kaɗai yana ƙara wa kwakwalwa lafiya da kuma taimakawa mutum daga kamuwa da cututtuka daban-daban, kamar yadda wani bincike ya gano.

‘Jam’iyyarmu ta APC na fuskantar barazanar faɗuwa a 2027’

'Jam'iyyarmu ta APC na fuskantar barazanar faɗuwa a 2027'

Alhamis 24 Yuli, 2025 da 4:01:48 Safiya

'’Ina hango mana kan cewa idan ba mu kawo sababbin tsari da muka jawo mutane suka ci gaba da tafiya da APC ba, za mu fuskanci abin kunya a zabe mai zuwa - 2027.’’

Yadda yanki mai arziƙin man fetur ya zama filin yaƙi a Sudan

Yadda yanki mai arziƙin man fetur ya zama filin yaƙi a Sudan

Alhamis 24 Yuli, 2025 da 4:04:10 Safiya

Iko da yankin Kordofan mai arziƙin man fetur wata babbar nasara ce ga ƙungiyoyin da ke faɗa da juna a yunƙurinsu na ƙwace ƙasar, in ji manazarta.

Jam’iyyar APC na gab da samun gagarumin rinjaye a majalisar ƙasar

Jam'iyyar APC na gab da samun gagarumin rinjaye a majalisar ƙasar

Laraba 23 Yuli, 2025 da 3:04:30 Yamma

A ranar Larabar nan ne ƴan majalisar dattawa guda huɗu da na wakilai guda uku suka sanar da sauya sheƙa daga jam’iyyar hamayya ta PDP zuwa mai mulki ta APC.

Majalisar dattawa ta amince da buƙatar Tinubu ta ciyo bashin dala biliyan 21

Majalisar dattawa ta amince da buƙatar Tinubu ta ciyo bashin dala biliyan 21

__

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/07/2025.

Abin da yarjejeniyar Amurka da Japan ke nufi ga Asiya da duniya

Abin da yarjejeniyar Amurka da Japan ke nufi ga Asiya da duniya

Laraba 23 Yuli, 2025 da 4:57:40 Yamma

Shugaban Amurka Donald Trump ya kira yarjejeniyar da ya cimma da Japan a matsayin “ta cinikayya mafi girma a tarihi.”

Shafin jana’izar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari

Shafin jana'izar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari

__

Shafin bayani kai-tsaye kan binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a ranar Talata 15 ga watan Yulin 2025.

Ko sarakuna na da rawar da za su taka a siyasar Najeriya?

Ko sarakuna na da rawar da za su taka a siyasar Najeriya?

Laraba 23 Yuli, 2025 da 11:22:26 Safiya

Kundin tsarin mulkin Najeriya bai fayyace takamaimiyar rawa da sarakunan za su iya takawa ba, amma a baya-bayan nan zargin shiga harkar siyasa dumu-dumu da ake yi wa sarakunan ya haifar da saɓani da lalacewar dangantaka tsakaninsu da ƴansiyasa.

Yadda mutum huɗu suka mallaki rabin dukiyar Afirka

Yadda mutum huɗu suka mallaki rabin dukiyar Afirka

Laraba 23 Yuli, 2025 da 4:01:04 Safiya

An kiyasta cewa kuɗin da mutanen ke da shi ya kai dala biliyan 57.4, sama da ɗaukacin duƙiyar ƴan Afirka miliyan 750, ko kuma rabin duƙiyar al’ummar nahiyar.

‘Sun kashe majinyata da ke kwance a gadon asibiti’ - BBC ta ji abin da ya faru a Suweida

'Sun kashe majinyata da ke kwance a gadon asibiti' - BBC ta ji abin da ya faru a Suweida

Laraba 23 Yuli, 2025 da 2:39:54 Yamma

BBC ta ziyarci Babban Asibitin Kasa na Suweida, inda ma’aikatan asibitin suka yi ikirarin an kashe marasa lafiya a kan gadajensu.

Illar da noman shinkafa ke yi ga muhalli

Illar da noman shinkafa ke yi ga muhalli

Laraba 23 Yuli, 2025 da 4:01:52 Safiya

Aƙalla mutum biliyan ke cin shinkafa a duniya. Ana dafawa a gidaje a kullum, sannan an fi rabawa a bukukuwa.

Amsoshin Takardunku: Kun san dalilin kafa hukumar nukiliya ta duniya da ma ayyukanta?

Amsoshin Takardunku: Kun san dalilin kafa hukumar nukiliya ta duniya da ma ayyukanta?

Lahadi 13 Yuli, 2025 da 2:34:29 Yamma

Shin me ya sa aka ƙirƙiri hukumar? kuma mene ne ayyukanta?

Ra’ayi Riga: Me ya sa yara a arewacin Najeriya suka fi kamuwa da tamowa?

Ra'ayi Riga: Me ya sa yara a arewacin Najeriya suka fi kamuwa da tamowa?

Lahadi 13 Yuli, 2025 da 2:04:00 Yamma

Jihohin da rahoton ya lissafa su ne Borno da Yobe da Kano da Katsina da Sokoto da Neja da Benue, inda rahoton ya ƙara da cewa lamarin ya shafi kashi 63 cikin 100 na ƙananan hukumomin jihohin.

Gane Mini Hanya: Ina PDP, amma zan yi aiki da haɗakar kayar da Tinubu - Sule Lamiɗo

Gane Mini Hanya: Ina PDP, amma zan yi aiki da haɗakar kayar da Tinubu - Sule Lamiɗo

Asabar 12 Yuli, 2025 da 10:19:06 Safiya

Ya ce ya amince ya yi aiki da haɗakar ne a wani yunƙuri na kawar da gwamnatin Tinubun a babban zaɓen ƙasar mai zuwa.

Lafiya Zinariya: Abubuwan da ke jawo wa mata ciwon kai

Lafiya Zinariya: Abubuwan da ke jawo wa mata ciwon kai

Asabar 12 Yuli, 2025 da 8:21:07 Safiya

Lafiya Zinariya: Wane yanayi jikin mace ke shiga da ke janyo mata ciwon kai?

Taɓa Kiɗi Taɓa Karatu 29/06/2025

Taɓa Kiɗi Taɓa Karatu 29/06/2025

Lahadi 29 Yuni, 2025 da 11:29:40 Safiya

Taɓa Kiɗi Taɓa Karatu, shiri ne da BBC Hausa ke kawo muku labarai na ban dariya da nishaɗi, da ban al’ajabi a wasu lokutan ma har da ban taƙaici.